Isa ga babban shafi
Wasanni

Ban ji dadin hukuncin da Chelsea ta yi min ba - Lampard

Frank Lampard ya bayyana rashin jin dadin matakin sallamarsa da Chelsea ta dauka, ba tare da ta bashi isasshen lokacin jagorantar ta zuwa samun nasarorin lashe kofuna ba.

Tsohon kocin Chelsea Frank Lampard
Tsohon kocin Chelsea Frank Lampard AFP
Talla

A jiya litinin Chelsea ta sanar da korar Lampard watanni 18 bayan kulla yarjejeniya da shi, saboda gaza lashe wasanni 5 cikin 8 na baya bayan nan da suka fafata a gasar Premier, duk da cewar ta kashe euro miliyan 220 wajen sayen ‘yan wasa a kakar wasa ta bana.

A halin yanzu tsohon kocin PSG Thomas Tuchel ake sa ran zai maye gurbin Lampard.

Mai horas da kungiyar Tottenham Jose Mourinho, wanda tsohon kocin Lampard ne, ya ce korar da Chelsea ta yiwa dalibin nasa ya nuna irin cin zalin hukumomin gudanarwa ko shugabannin kungiyoyin kwallon kafa da ya zama ruwan dare a wannan zamani.

A cewar Mourinho baya jin dadi a duk lokacin da wani mai horaswa ya rasa aikinsa ballanta Lampard da ya bashi gudunmawa matuka lokacin da ya horas da Chelsea.

A makon jiya shi ma kocin Arsenal Mikel Arteta ya ce koka kadan ba ya jin dadin yadda Lampard ke fuskantar kalubalen rashin nasarori.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.