Isa ga babban shafi
Wasanni

"'Yan wasan Manchester City mugaye ne"

Kocin Manchester United Ole Gunnar Solskjaer ya gargadi ‘yan wasansa da su shirya shan maka daga ‘yan wasan Manchester City a karawar da za su yi yau a Old Trafford, kalaman da suka bai wa Pep Guardiola mamaki, ganin yadda takwaransa ya alakanta ‘yan wasansa da mugunta.

Wasu daga cikin 'yan wasan Manchester City
Wasu daga cikin 'yan wasan Manchester City Reuters
Talla

Solskjaer ya ce, za a yi wa ‘yan wasansa mugunta ta hanyar dukan kafafunsu a karawar, sai dai Guardiola bai ji dadin wannan furuci ba, yana mai cewa, ba a horar da ‘yan wasansa akan irin wannan dabi’a ba.

A can baya, an zargi Guardiola da yi wa 'yan wasan hudubar yi wa abokan karawarsu mugunta cikin dabara, zargin da ya musanta.

A bangare guda, Guardiola ya ce, a yanzu, gidan Manchester United wato Old Trafford, ba wurin da za a ji tsoron ziyarta bane, sabanin shekarun baya da ake fargabar kai mata ziyara.

Muddin Manchester City ta yi nasara a wasan na yau, hakan zai dada kara mata kwarin guiwar ci gaba da rike kambin firimiyar Ingila.

Alkaluma sun nuna cewa, Manchester City ta samu nasara a wasanni biyar daga cikin bakwai da ta buga a Old Trafford a baya-bayan nan.

A karon farko tun shekarar 1989, Manchester United ta yi rashin nasara a wasanni shida daga cikin takwas da ta buga a gasa daban daban a baya-bayan nan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.