UEFA ta bai wa Jamus izinin gudanar da EURO 2024
Kasar Jamus ta doke Turkiya a fafutukarsu ta neman izinin karbar bakwancin gasar cin kofin kasashen nahiyar Turai ta 2024, wato EURO 2024 bayan kwamitin gudanarwar hukumar ya kada kuri’a.
Wallafawa ranar:
An gudanar da zaman kada kuri’ar ne a birnin Nyon na kasar Switzerland a ranar Alhamis bayan kasashen biyu sun gabatar da yunkurinsu na karshe kan batun.
A karon farko kenan da Jamus za ta gudanar da wannan gasar tun bayan hadewarta da Jamus ta Yamma wadda ta karbi bakwancin gasar a shekarar 1988.
Kawo yanzu, Turkiya ba ta samu damar daukan nauyin wata babbar gasar kwallon kafa ba duk da kokarin da ta yi a shekarun 2008 da 2012 da 2016 na ganin ta karbi bakwancin gasar ta Turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu