Akwai bukatar masoyan Arsenal su cigaba da goya mana baya - Wenger
Mai horar da Arsenal Arsene Wenger, ya bukaci magoya bayan kungiyar da su cigaba da mara musu bay aba tare da faduwar gaba ba.
Wallafawa ranar:
Kiran na Wenger, yazo ne bayan lallasa Arsenal da Liverpool ta yi da kwallaye 4 – 0, wasan da Wenger ya bayyana shi a matsayin iftila’I ga Klub din.
A lokacin wasan da aka fafata a jiya dai, an jiyo magoya bayan kungiya suna karajin ya kamata a kori Wenger.
To sai dai bisa dukkanin alamu a bangaren Wenger, kiraye-kirayen aikin banza ne wai an jefa agwagwa a ruwa, domin bayanda aka tambaye shi kan mai zai ce dangane da hakan, sai ya kada baki ya ce, aci gaba da hakuri da shi, idan har shi ne matsalar Arsenal, amma fa bai kamata masoya su juya musu baya ba, duk da shan kashin da suka yi, a karo na gaba rama abinda kungiyar ta Liverpool ta yi musu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu