Isa ga babban shafi

A Gabon za a yi gasar Afrika duk da tarzoma- CAF

Hukumar kwallon kafar Afrika CAF ta ce za a yi wasannin gasar cin kofin Nahiyar a Gabon duk da kasar ta fada cikin rikicin siyasa bayan sake zaben shugaba Ali Bongo.

Rikici ya barke a Gabon bayan sanar da Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa
Rikici ya barke a Gabon bayan sanar da Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa REUTERS/Life Africa TV
Talla

CAF ta ce ba wani sauyi kuma za ta ci gaba da shirye shiryen karbar bakuncin gasar.

Gabon dai za ta dauki nauyin wasannin ne a tsakanin 14 ga watan Janairu zuwa 5 Fabrairu.

A Libya ya kamata a gudanar da gasar amma saboda rikicin da ake yi a kasar aka janye aka ba Gabon.

CAF ta ce shirin hada kasashen da za su kara a rukunin farko na nan kamar yadda aka tsara a ranar 19 ga watan Oktoba a birnin Libreville.

Sai dai kakakin hukumar Junior Binyam ya ce ana iya samun sauyi amma hakan ya dogara ne da sakamakon babban taron da CAF za ta gudanar Al Kahira a ranar 21 ga watan Satumba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.