A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Intanet, hukumar FIFA ta tuna da kwallon da Yekini ya jefa a ragar kasar Bulgaria a gasar cin kofin duniya da aka gudanar a Amurka a shekara ta 1994.Wannan kwallon dai, ita ce ta farko da Najeriya ta ci a gasar cin kofin duniya, yayin da Yekini ya shiga cikin ragar yana girgizata, yana kuka domin nuna farin cikinsa na zura wannan kwallo mai cike da tarihi.Ya dai rasu a ranar 4 ga watan mayun shekarar 2012 bayan ya yi fama da rashin lafiya. Sannan ya bar duniya yana da shekaru 48 da haihuwa.Ramatu Garba Baba ta yo mana dubi a kai tareda kawo wasu labaren wasanni a cikin shirin Duniyar Wasanni.
Sauran kashi-kashi
-
Har yanzu akwai rashin tabbas game samar da ingantaccen tsaro yayin gasar Olymics mai zuwa
Shirin duniyar wasanni na wannan mako ya dubi yadda ake tufka da warwarwa game da tsarin samar da cikakken tsaro yayin gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta Olympics da birnin Paris zai karbi bakunci.06/05/202409:59 -
Hasashen yadda za ta kaya a gasar Firimiyar Ingila
Shirin a wannan lokaci ya fi karkata akalar ne kan gasar Firimiyar Ingila, wadda ke ci gaba da jan hankali, duk da shawo gangarar da akayi.15/04/202409:59 -
Ci gaban da aka samu a wasan damben gargajiya a Najeriya
Shirin 'Duniyar Wasanni' na wannan makon tare da Khamis Saleh ya maida hankali ne kan irin ci gaban da aka samu a bangaren wasan damben gargajiya a Najeriya.11/03/202409:59 -
Yadda aka kammala zangon farko na gasar kwallon kafa ta Firimiyar Najeriya
Shirin awanan lokaci zai nazari game da yadda zangon farko na gasar Firimiyar Najeriya ya kammala, inda tuni aka juya zagaye na biyu na gasar ta kwararru.Shirin ya kuma duba batun soma gasar a kan lokaci da kuma batun daukar nauyi, sai kuma batun rashin ingancin filaye, baya ga kuma karanchin samun bayanan ‘yan wasan da ke taka leda a gasar.Latsa alamar sauti don sauraron shirin:04/03/202410:00 -
Yadda Ivory Coast ta lashe kofin AFCON bayan ta doke Najeriya
A daren jiya Lahadi ne aka kammala gasar lashe kofin Afrika AFCON karo na 34 da Ivory Coast ta karbi baukunci kuma daga bisa ta lashe gasar. Najeriya ce ta fara zura kwallon farko ta hannun William Ekong tun kafin a tafi hutun rabin lokacin, sai dai bayan dawowa ne tawagar ta Elephants ta farke ta hannun Kesse kafin daga bisani a minti na 81 ta kara kwallo ta hannun Sebestin Hallar wacce ta bata nasara.12/02/202409:58