Van Gaal ya fusata da tambayoyin 'yan jarida
Kocin kungiyar kwallon kafa ta Manchster United Louis Van Gaal ya fice daga zauren taron manema labarai cikin fushi da aka gudanar a jiya laraba bayan amsa tambayoyi uku kacal.
Wallafawa ranar:
Van Gaal mai shekaru 64 da haihuwa bai ji dadin tambayoyin da 'yan jarida suka yi masa ba game da makomarsa a Manchester United yayin da ake ta rade radinn cewa da yiwuwar kungiyar ta raba gari da shi.
An gudanar da taron 'yan jaridan ne gabanin wasan da Manchester United za ta yi a ranar asabar da Stoke City kuma tsawon minti 5 kacal aka shafe a taron kafin Van Gaal ya fice.
Sannan ya ce, shi fa ya halarci taron ne domin amsa tambayoyi dangane da dokokin gasar Premier ta Ingila amma ba akan makomarsa.
Manchester United dai ta yi rashin nasara a wasanni shida da ta yi yayin da ta sha kayi a wasanni guda uku na baya bayan nan da ta yi da Wolfsburg da Bournemouth da kuma Norwich.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu