Najeriya ta doke Brazil a Chile
‘Yan wasan Golden Eaglets na Najeriya sun kai zagayen kusa da karshe a gasar cin kofin duniya ta ‘yan kasa da shekaru 17 da ake gudanarwa a Chile, bayan sun lallasa ‘yan wasan Brazil 3 da 0.
Wallafawa ranar:
Tun kafin a je hutun rabin lokaci ‘yan wasan Eaglets suka ba Brazil kashi.
Victor Oshimen ne ya fara zira kwallo a raga ana minti 28 da fara kwallo, kuma kwallon shi ta 8 da ya zira a gasar.
Bayan minti guda kuma Kingsley Michaely Michael ya sake jefa kwallo ta biyu. Can daga bisani kuma kafin aje hutun rabin lokaci Udochukwu Anumudu ya zira kwallo ta uku ana minti 34 da wasa.
Yanzu Golden Eaglets za su hadu ne da Ecuador ko Mexico a ranar Alhamis a wasan dab da na karshe wadanda za su kece raini a yau Litinin.
Bidiyon yadda Golden Eaglets suka lallasa Brazil
ICYMI: The Golden Eaglets roared into the semi-finals as they thrashed Brazil. Watch #SoarGoldenEaglets pic.twitter.com/fTNpiKcodA
— The NFF (@thenff) November 2, 2015
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu