Gwamnatin Jihar Kano ta yiwa ‘yan wasan Golden Eaglets goma ta arziki
Gwamnatin Jihar kano ta karrama ‘yan wasan Golden Eaglets da suka lashe gasar cin kofin duniya ta ‘yan kasa da shekaru 17 a jiya Talata inda ta yiwa kowane dan wasa alkawarin kudi naira 300,000.00 yayin da mai horar da su, Manu Garba zai samu 500,000.00.
Wallafawa ranar:
Gwamnan Jihar Rabiu Musa Kwankwaso wanda ya bayyana hakan a wani bikin karrama ‘yan wasa da aka shirya ya yiwa ‘yan asalin kano dake tawagar kungiyar su biyu, wato Zahraddeen Bello da Musa Muhammad alkwarin gidaje.
Haka zalika za a saka sunayen ‘yan wasa a wasu titunan birnin na Kano.
A baya gwamnatin tarayya ta karrama ‘yan wasan da kyautar kudi miliyan biyu –biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu