Isa ga babban shafi
Beijing

Kenya ta samu yawan lambobin yabo a Beijing

Shugaban Kenya Uhuru Kenyatta ya jinjinawa ‘Yan wasan kasar kan rawar da suka taka na lashe yawan lambobin yabo a wasannin guje guje da tsalle tsalle na duniya da aka kammala a Beijing.

Joyce Zakary ta Kenya da ta lashe tseren gudun Mita 400 a Beijing
Joyce Zakary ta Kenya da ta lashe tseren gudun Mita 400 a Beijing Reuters/David Gray
Talla

Wannan ne karon farko da Kenya ta zo a matsayi na farko da yawan lambobin yabo inda ta lashe guda 16 da suka hada da zinariya 7.

Kenya ta sha gaban Jamaica da ta zo a matsayi na biyu da kuma Amurka a matsayi na uku.

Kenya dai ta samu nasarar ne a tseren gudu mai nisan zango.

Birtaniya ce ta zo a matsayi na hudu sai kuma Habasha daga Afrika a matsayi na biyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.