Cristiano Ronaldo yace a Madrid zai yi ritaya
Cristiano Ronaldo yace ba zai bar Real Madrid ba tsawon rayuwar shi. Dan wasan ya fadi haka ne a wata Hira da ya yi da Jaridar Wasanni ta Marca a Spain bayan ya lashe kofin La liga na Farko bana.
Wallafawa ranar:
“Zan yi Ritaya a Real Madrid” inji Christiano wanda ya fara taka kwallo a shekarar 2009 da Real Madrid bayan ya baro Manchester United.
Ronaldo yace akwai yiyuwar zai kwashe tsawon shekaru 10 da Karin wasu sama a Benabeur. Domin a cewarsa Rayuwar shi na tafiya dai dai a Spain.
A bana dai Ranaldo yana fatar lashe kyautar kwarzon dan wasan Duniya karo na biyu bayan ya lashe kyautar a lokacin da yana Manchester United. Sai dai an kwashe shekaru uku Lionel Messi yana haramtawa dan wasan kyautar. Kuma ko a bana akwai yiyuwar Messi zai iya lashe kyautar idan har Ronaldo bai yi komi ba a Euro da Olympics.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu