Isa ga babban shafi
Kwallon kafa

Libya da Mali sun sha gaban Najeriya da Masar a fagen tamola

A ajin matsayi a duniya da hukumar FIFA ta fitar, kasar Jamus ta karbe matsayi na biyu daga hannun Holland, amma kasar Spain ce har yanzu a matasayi na daya a duniya, kasar Hollad ta koma matsayi na hudu amma Uraguay ce a matsayi na uku.

Dan wasan kasar Cote d'Ivoire Didier Drogbalokacin da yake murnar zira kwallo a ragar Mali a wasan kusa da karshe a gasar cin kofin Afrika
Dan wasan kasar Cote d'Ivoire Didier Drogbalokacin da yake murnar zira kwallo a ragar Mali a wasan kusa da karshe a gasar cin kofin Afrika Reuters/Louafi Larbi
Talla

A Nahiyar Afrika, Kasar Cote d’IVoire ce ke jagorancin kasashen a matsayi na daya amma matsayi na 15 a duniya. Kasar Ghana ce a matsayi na biyu amma ta 22 a duniya.

Kasashe irinsu Libya da Algeria da Mali da Gabon dukkaninsu suna gaban Najeriya da Masar da Africa ta kudu.

Domin Algeria ce a matsayi na uku, Mali a matsayi na hudu Zambia a matsayi na biyar Gabon a matsayi na shida Libya a matsayi na Bakwai.

Kasar Masar ce a matsayi na Takwas amma ta 55 a duniya. Najeriya kuma a matsayi na 10 a Afrika amma ta 60 a duniya.

 

Jerin matsayi a Nahiyar Afrika da hukumar FIFA ta fitar a ranar 11 ga watan Afrilu.

15 1 Côte d’Ivoire

22 2 Ghana

38 3 Algeria

39 4 Mali

40 5 Zambia

42 6 Gabon

46 7 Libya

55 8 Masar

57 9 Tunisia

60 10 Najeriya

71 15 Afrika ta Kudu

102 23 Malawi

107 28 Botswana

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.