Isa ga babban shafi
Kwallon kafa

Zambia zata buga wasan karshe tare da tuna ‘yan wasanta da suka mutu

Kasar Zambia zata buga wasan karshe a gasar cin kofin Afrika da kasar Cote d’Ivoire tare da tuna tsuffin ‘yan wasanta da suka mutu a wani hadarin jirgin sama a Gabon a shekarar 1993. A Malabo kuma a gobe Assabar Ghana da Mali zasu Fafata domin neman matsayi na uku.

'Yan wasan kasar Zambia lokacin da suke kai ziyara wajen da 'Yan wasan kasar suka yi hadarin jrigin sama a kasar Gabon shekarar 1993.
'Yan wasan kasar Zambia lokacin da suke kai ziyara wajen da 'Yan wasan kasar suka yi hadarin jrigin sama a kasar Gabon shekarar 1993. REUTERS/Thomas Mukoya
Talla

Bayan zuwansu birnin Libreville ne inda zasu kara da Cote d’Ivoire, ‘Yan wasan Copper bullet suka kai ziyara wurin da jirgin sama ya yi hadari da daukacin ‘yan wasan kasar, a lokacin da suke kan hanyarsu zuwa buga wasan neman shiga gasar cin kofin duniya da Senegal a birnin Dakar.

mutane 30 ne a cikin jirgin, ‘Yan wasa 25 da matuka 5 dukkaninsu suka mutu. A lokacin dai dan wasan Zambia daya ne hadarin bai rutsa da shi ba, waton Kalusha wanda shi ne gwarzon dan wasan Afrika a Lokacin wanda ke taka leda a kasar Holland kungiyar PSV Eindhoven, kuma shugaban hukumar kwallon kafar kasar na yanzu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.