Isa ga babban shafi
Kwallon kafa

Gabon da E/Guinea sun zama ‘yan kallo a gasar Cin kofin Afrika

kasar Ghana da Mali da Cote d’Ivoire da Zambia sun tsallake zuwa wasan kusa `da karshe. Mali da Cote d’Ivoire ne suka sallami masu daukar nauyi gasar Gabon da Equatorial Guinea a wasan quarter final.

Dan wasan kasar Cote d'Ivoire  Didier Drogba a Lokacin da suke karawa da kasar Equartorial guinea
Dan wasan kasar Cote d'Ivoire Didier Drogba a Lokacin da suke karawa da kasar Equartorial guinea REUTERS/Luc Gnago
Talla

A ranar Assabar ne kasar Cote d’IVoire ta doke Equatorial Guinea ci 3-0.

A jiya Lahadi ne kasar Mali ta doke Gabon a bugun daga kai sai mai tsaron gida bayan kammala mintinan wasan ana kunnen doki ci 1-1. Didier Drogba wanda ya zira kwallaye biyu a wasan Cote divoire da Equatorial Guinea yana a babban birnin kasar Gabon lokacin da aka fitar da kasar a gasar.

‘Yan wasan Black Stars na Ghana sun doke Tunisia ne ci 2-1 duk da cewa alkalin wasa ya ba d an wasan Ghana Jan kati.

Yanzu haka a ranar Laraba kasar Ghana zata fafata da Zambia wacce ta doke kasar Sudan a wasan Quarter final.

Cote d’Ivoire kuma zata kara ne da kasar Mali.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.