Isa ga babban shafi

Faransa ta karbi bakin da suka yi ta gararamba a teku

Bayan share tsawon kwanaki ana gararamba da su a kan teku cikin wani jirgin ruwan agaji mai suna Ocean Viking, a safiyar yau juma’a ‘yan ci-rani 230 sun sauka a tashar jiragen ruwan Toulon da ke kudancin Faransa.

The humanitarian ship the Ocean Viking makes its way into the military base in Toulon, France, Friday, Nov. 11, 2022. The Norwegian-flagged vessel, operated by the NGO SOS Méditerranée, had been at sea for nearly three weeks carrying around 230 migrants. Italy had refused to allow the migrants to disembark on Italian territory. (AP Photo/Daniel Cole)
The humanitarian ship the Ocean Viking makes its way into the military base in Toulon, France, Friday, Nov. 11, 2022. The Norwegian-flagged vessel, operated by the NGO SOS Méditerranée, had been at sea for nearly three weeks carrying around 230 migrants. Italy had refused to allow the migrants to disembark on Italian territory. (AP Photo/Daniel Cole) AP - Daniel Cole
Talla

Jirgin ruwan wanda wata kungiyar agaji ta Faransa ke kula da ita, ta kwaso bakin hauren ne daga gabar ruwan Libya, kafin a dauki tsawon makwanni ana neman tashar jiragen ruwan da za ta karbe su.

Gabanin wannan lokaci dai, Faransa ba ta taba barin wani jirgin ruwa dauke da bakin haure daga Tekun Mediterranean sauka a gabarta ba, amma a wannan karon ta amince da haka saboda kasar Italiya ta ki karbar bakin.

Tuni Firaministan Italiya Giorgia Meloni ta soki gwamnatin Faransa kan yadda ta karbi bakin da ta ce Rome ta ki amincewa da su.

Tun da fari, gwamnatin Faransa ta ce, Italiya ce ke da alhakin karbar bakin amma ta yi biris, kuma wannan al'amari shi ne rikicin baya-bayan tsakanin kasashen biyu game da matsalar bakin haure da ke balaguro zuwa Turai daga nahiyar Afrika.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.