Francois Hollande zai yi jawabi game da harin ta'addancin da aka kai Paris
Tsohon shugaban Faransa Francois Hollande zai amsa tambayoyi dangane da yadda wani kwamandan masu jihadi ya kitsa kai harin ta'addanci a Paris ba tare da an gano shi ba tun da fari.
Wallafawa ranar:
Tsohon shugaba Francois Hollande ya shugabanci Faransa tsakanin shekara ta 2012 zuwa 2017.
A lokacin wannan hari Francois Hollande na halartan kallon wasannin sada zumunci ne na kwallon kafa tsakanin Faransa da Jamus a Paris, a lokacin da ‘yan ta'addan suka fara sakin bamabamai, al’amarinda ya sa jami'an tsaron tattara shugaban kasar zuwa tudun mun tsira.
Daga bisani ne kuma wasu ‘yan bindiga suka yi ta bude wuta kan mai tsautsayi.
Mutane akalla 130 ne aka lissafa sun rasa rayukansu a harin ta'addanci na ranar 13 ga watan Nuwamba, 2015.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu