Isa ga babban shafi
Faransa

Macron zai ci gaba da sauye-sauye duk da tarzomar da ake yi

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce zai ci gaba da aiwatar a sauye-sauyen da ya fara daga lokacin da aka zabe shi, domin kuwa abubuwa ne da al’ummar kasar ke bukata, duk da cewa a daya bangaren an share tsawon watanni biyar ana gudanar da tarzomar nuna adawa da wasu daga cikin manufofinsa na siyasa a kasar.

Emmanuel Macron 26-04-2019
Emmanuel Macron 26-04-2019 REUTERS/Philippe Wojazer
Talla

Macron wanda ke gabatar da jawabin da aka jima ana dako, a wannan alhamis ya ce manyan manufofin siyasa da gwamnatinsa ta fara aiwatarwa cikin shekaru da suka gabata, sun dace da bukatun al’ummar kasar.

To sai dai shugaban ya ce a shirye yake ya yi sassaucin biyan haraji a kan Faransawa, kamar dai yadda ya dauki irin wannan alkawari a tsakiyar watan nuwambar da ya gabata.

A wani bangare na jawabinsa, shugaba Emmanuel Macorn ya bayyana nadama dangane da yadda a wasu lokuta ya kasance mai tsanantawa a matakan da yake dauka kan al’ummar kasar.

An dai share tsawon watanni biyar ana tarzoma a sassan kasar ta Faransa, inda jama’a ke nuna rashin amincewa da wasu manufofin shugaban, musamman na batutuwan da suka shafi tattalin arziki da shugaban ke dauka a cikin gida, yayin da wasu ke bayyana shi a matsayin wanda ke kokarin kare muradun attajirai da manyan kamfanonin duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.