Isa ga babban shafi
Faransa

Dan bindiga ya bude wuta kusa da Masallaci a Faransa

Wani dan bindiga ya buda wuta tare da raunata mutane 8 a kofar wani masallaci da ke garin Avignon da ke kudancin Faransa, al’amarin da mai shigar da kara na gwamnati ya nisanta da ayyukan ta’addanci.

An taba kai hari a Masallacin Créteil, da ke Paris a Faransa
An taba kai hari a Masallacin Créteil, da ke Paris a Faransa REUTERS/Gonzalo Fuentes
Talla

‘Yan sanda sun ce da misalin karfe 10 da rabi na daren jiya ne wasu mutane biyu cikin wata mota suka buda wuta a kofar masallacin, inda yanzu haka ake ci gaba da farautar maharan.

Harin na zuwa kwanaki bayan wani mutum ya abka wa masu ibadah a masallacin Cretail kudancin Paris a ranar Alhamis.

Al’ummar musulmi a Faransa sun bayyana damuwa akan yadda ake kokarin kai masu hari a wajen ibadah inda suka yi kira ga mahunkunta wajen tabbatar da tsaro musamman a masallatai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.