Isa ga babban shafi
Jamus-Saudia

Merkel, ta kai ziyarar aiki ga sarki Salman na Saudia

A yau lahadi, Waziriyar Jamus Angela Merkel ta ziyarci kasar Saudi Arabiya, ziyarar da aka sadaukar kan huldar dake tsakanin Berlin da katafariyar masarautar mai arzikin man fetur a duniya.

waziriyar jamus  Angela Merkel  06 03 2017.
waziriyar jamus Angela Merkel 06 03 2017. REUTERS/Fabrizio Bensch
Talla

Wannan ziyara dai tazo ne a yayinda ake shirin gudanar da zaman taron kungiyar G20 ta kasashe masu karfin tattalin arziki su 20 a watan yulin wannan shekara a Hambourg na kasar Jamus, kamar yadda majiyar diflomasiyar Jamus ta sanar.

Jim kadan bayan isarta a birnin Jedda dake yammacin kasar ta Saudiya, Merkel ta samu tarbe daga sarki Salman daya daga cikin manyan abukan kawancen jamus.

Wata majiyar ta ce, shuwagabannin 2 sun tattauna ne, kan maudu’an da zaman taron gugun g20 zai maida hankali a kai, wadanda suka hada da maganar yaki da dumamar yanayi, da kuma ta makamashi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.