'Yan takarar shugabancin Faransa na ci gaba da jawarcin masu zabe
Yayin da ya rage kwanaki 10 a gudanar da zagaye na biyu na zaben shugabancin kasar Faransa, ‘yan takara a wannan zabe Marine Le Pen da Emmanuel Macron na ci gaba da jawarcin jama’a domin samun kuri’unsu a zaben na ranar 7 ga watan gobe.
Wallafawa ranar:
Le Pen na gudanar da taron gangami ne a garin Nice a wannan alhamis, yayin da Macron ke shirin zantawa da manema labarai a wata hira da za a watsa gidan talabijin dangane da manyan manufofinsa.
A jiya laraba mutanen biyu sun gudanar da yakin neman zabensu ne a Amiens, yankin da ake kallo a matsayin muhimmi ga Le Pen sakamakon dimbin kuri’un da ta sama a zagayen farko na zaben.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu