Tattaunawar kawo karshen zanga-zanga a Guyane
An soma tattaunawar neman mafita a zanga zangar da ta barke a Guyane, daya daga cikin tsibiran utr-mer dake karkashin kasar Faransa.Gwamnatin Faransa ta tura da ministan dake kula da tsibiran Ericka Bareigts wanda ya nemi gafarar mutan tsibirin da suka bukaci kara inganta rayuwarsu kamar na sauran yankunan kasar ta Faransa.
Wallafawa ranar:
Talakawa masu zanga zangar na bukatar ganin gwamnatin Faransa ta dau halin da suke ciki da muhimmanci, musaman wajen magance matsalar talauci da rashin aikin yi da ake fama da shi.
Yanzu haka zababbun yankin sun gabatar da bukatun magancewa al’ummominsu matsalolin da suke fama dasu ga yan takarar shugabancin kasar.
Kudaden shiga da na harajin da yankunan ke samu domin gudanar da ayyukan ci gaban rayuwar jama’a sun kankance a ya yin da kudaden da gwamantin faransa ke ware masu kuma suka yi kasa
Gwamnatin Faransa ta sanar da ware kusan bilyan daya na euro a matsayin tallafi,shawarar da masu zanga-zangar suka nuna adawa a kai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu