Isa ga babban shafi
Birtaniya

May ta nada sabbin ministocin Birtaniya

Sabuwar Firaminsitar Birtaniya Theresa May ta nada Boris Johnson a matsayin ministan harkokin wajen kasar bayan ta kama aiki a jiya Laraba.

Theresa May ta fara sabuwar raywa a gidan gwamnatin Birtaniya da ke lam ba 10 a downing street
Theresa May ta fara sabuwar raywa a gidan gwamnatin Birtaniya da ke lam ba 10 a downing street REUTERS/Stefan Rousseau/Pool
Talla

Mr. Johnson ya kasance jigo wajen ganin al’ummar Birtaniya sun kada kuri’ar ficewa daga kungiyar tarayyar Turai a zaben raba gardamar da suka kada a cikin watan jiya.

Mr. Johnson wanda tsohon magajin garin London ne, ya maye gurbin Philips Hammond wanda ya rike mukamin ministan harkokin waje a gwamnatin David Cameron.

To sai dai shi ma Hammond za a dama da shi a sabuwar gwamnatin, inda a yanzu May ta nada shi ministan kudi sakamakon goyon bayan da ya nuna mata.

Har ila yau, an nada Amber Rudd a matsayin ministan harkokin cikin gidan Birtaniya yayin da aka bar Michael Fallon akan mukaminsa na ministan tsaro.

Kazalika, Misis May ta nada David Davis a matsayin ministan da zai kula da shirin ficewar Birtaniya daga tarayyar turai kuma a karon farko kenan da aka kirkiri wannan kujerar a Birtaniya.

Ana saran nan gaba kadan za ta nada ministocin lafiya da ilimi da kuma ayyuka da harkokin kasuwanci.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.