Beljiyom ta kara karfafa matakan tsaro a tashoshin jiragen kasanta...
Gwamnatin kasar Beljiyom a yau assabar ta yanke karfafa matakan tsaro a tashoshin jiragen kasanta bayan faruwar harin da wani mutum dake dauke da makamai ya kai a jiya juma’a a cikin wani jirgin kasa a Thalys
Wallafawa ranar:
Ofishin dake yaki da ayukan ta’addanci kasar Spain ya bayyana cewa, mutumen da aka kama a lokacin hari jirgin na Thalys da ke zuwa biranen Amsterdam-da Paris, da zama dan wata kungiyar mayakan islama a kasar Syriya da kuma ke zaune a faransa.
Yanzu dai ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano ko yana tare da wasu da ke ci gaba da buya a Fransa ko kuma a kasar ta Beljiyom
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu