Isa ga babban shafi
Tarayyar Turai

Le Pen zata jagoranci adawa a Turai

Bayan kammala zaben majalisar kasar Turai , Shugabar Jamiyyar National Front a kasar Faransa Marine Le Pen tace tana da kyakyawan burin ganin ta hada kan masu ra’ayinsu a majalisar.

Marine Le Pen Jagorar Jam'iyyar kishin kasa ta Faransa tare da wasu 'Yan adawa a Brussels
Marine Le Pen Jagorar Jam'iyyar kishin kasa ta Faransa tare da wasu 'Yan adawa a Brussels REUTERS/Francois Lenoir
Talla

Bayan nasarar samun kashi 25% na kuri’u daga kasar Faransa, Marine Le Pen ta bayyana gaban manema labarai a Brussels tare da masu ra’ayi daya daga kasashe hudu. Le Pen ta bayyana cewa sun damu matuka game da ci gaban kungiyar Turai a nan gaba.

Idan dai aka amince da kungiyar su a majalisar ta Turai, bangarorin masu ra’ayin kishin kasa za su yi nasarar gabatar da ra’ayinsu a majalisar ba tare da jibin goshi ba, kuma suna iya rike shugabancin kwamiti daga cikin kwamitoci 20 na majalisar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.