Isa ga babban shafi
Faransa

Ana ci gaba da farautar mutumin da ya kashe sojan Faransa

Jami’an tsaro na ci gaba farautar wani mahari da ya soke sojin kasar Faransa da wuka a wani lungun hada hadar kasuwanci a kasar ta Farnsa.Wani jami’in ‘yan sandan, ya bayyana cewar jami’ai masu kula da ayukan ‘yan ta’adda nacan suna aiki babu kama hannun Yaro domin zakulo wanda yayi wannan aika-aikar.Sai dai shugaba Francios Hollande ya bayyana cewar, ya zuwa yanzu ba zasu alakanta harin da wanda aka kaiwa sojin kasar Burtaniya a cikin makon day a gabata ba.Sojan da aka kashe, dake dauke da Bindiga cikin kaki, na aikin Sintiri ne daga cikin Sojin da aka sa domin gano maboyar ‘yan ta’adda a kasar.Maharin da aka bayyana shi a matsayin dan shekara 23 ya bace ko-sama-ko-kasa. 

Shugaban Faransa François Hollande
Shugaban Faransa François Hollande REUTERS/Benoit Tessier
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.