Hollande ya yi tir da harin da aka kai wa Traore a Mali
Shugaban Faransa Francois Hollande ya yi Allah waddai da harin da masu zanga zanga suka kai wa shugaban riko na kasar Mali, Dioncounda Traore, inda suka mi shi duka tare da neman shugaban ya yi murabus.
Wallafawa ranar:
Lamarin ya zo ne kwana guda, bayan da wakilan kungiyar hadin kan tattalin arzikin yankin Afrika ta Yamma ECOWAS ko CEDEAO suka kulla wata yajejeniya da sojojin da suka kifar da gwamnatin farar hulan kasar.
Kamar yadda aka tsara yarjejejniyar, Traore zai jagoranci gwamnatin rikon kwarya tsawon watanni 12, kafin ya mika mulki ga zababbiyar gwamnatin farar hula.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu