Isa ga babban shafi
Faransa-Jamus

Hollande da Merkel sun yi alkawalin yin aiki tare don ci gaban Turai

Shugaban Kasar Faransa, Francois Hollande, tare da takwararsa ta kasar Jamus, Angela Merkel, sun yi alkawarin aiki tare, don ganin sun magance matsalolin da ke addabar kudin euro da kuma tattalin arzikin Turai.

Angela Merkel da François Hollande,a lokacin da suke ganawa a birnin à Berlin, bayan rantsar da Hollande matsayin sabon shugaban kasa
Angela Merkel da François Hollande,a lokacin da suke ganawa a birnin à Berlin, bayan rantsar da Hollande matsayin sabon shugaban kasa REUTERS/Jacky Naegelen
Talla

Bayan ganawar da suka yi ta farko a Berlin, jim kadan bayan rantsar da sabon shugaban, shugabanin biyu sun tattauna kan banbancin ra’ayin da ke tsakaninsu.

Wannan ita ce ziyarar Francois Hollande ta farko a matsayin Shugaban kasar Faransa.

An dai yi has ashe za’a tashi baran-baran tsakanin shugabannin biyu saboda sabanin ra’ayi game da matsalar tattalin arzikin Turai amma a lokacin da suke ganawa shugabannin sun yi kokarin hada kai domin samun daidaito.

A lokacin da yake jawabi, Hollande yace Jamus da Faransa zasu hada kai domin samar da ci gaba a Nahiyar Turai.

Shugabannin biyu sun bayyana fatansu wajen ganin dorewar kasar Girka a kungiyar kasashe masu amfani da kudin euro.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.