Isa ga babban shafi
Jamus

Takaddama ta kaure a Jamus bayan wasu sun yi kokarin raba Qur’ani

Hukumomin Kasar Jamus sun nuna damuwarsu game da yadda wata kungiyar addinin Islama ke yunkurin raba kur’ani Miliyan 25 ga jama’ar kasar Abinda gwamnati tace cin zarafin littafi mai Tsarki ne.

Wata Yarinya tana karnata wani bangare na Al Qaur'ani
Wata Yarinya tana karnata wani bangare na Al Qaur'ani REUTERS/Zohra Bensemra
Talla

Shugaban gwamnatin Jamus Angela Merkel ta yi Allah waddai da wannan yunkuri na raba Al Qur’ani mai girma wanda aka rubuta cikin harshen Jamusanci.

Wannan al’amarin ya janyo Muhawara tsakanin ‘Yan siyasan kasar.

Sai dai masu raba Qur’anin suna ganin ya kamata a girmama ‘Yancin addini a kasar.

Kodayake wasu kungiyoyin addinin Islama sun soki wanan yunkuri da yan salafiya ke kokarin yi abinda yasa gwamnatin kasar son sanin inda kudin raba Al Qur’ani ya fito.

Kungiyar salafiyya masu ikirarin addinin gaskiya sun sha alwashin raba Al Qaur’ani ne a kan titunan kasashen Jamus, Austria, Switzerland tare da watsa wasu a Intanet don cim ma manufarsu na musuluntar Jama’a, abinda gwamnati ta kira hanyar haifar da jahadi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.