Spain-Mali-Mauritania
Wadanda kungiyar Al Qaeda ta sake sun koma gida
YAN Kasar Spain biyu da kungiyar Al Qaeda ta sake, bayan garkuwa da sun a watanni tara, sun koma kasar su.Mutanen biyu, Roque Pascual da Albert Vilalta, da aka sace a kasar Mauritania, sun isa Barcelona, inda suka samu tarba daga Yan uwa da abokan arziki.Prime Ministan kasar, Jose Luis Rodriquez Zapatero, ya bayyana farin cikinsa da samun kan mutanen, wadanda ya ce sun fuskanci mawuyacin hali, yayin da suke hannun wadanda sukayi garkuwa da su.Bayyanai daga kungiyar ta Al Qaeda, sun nuna cewar, Spain ta biya makudan kudade, kafin sakin ma’aikatan agajin.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: