Hukumar hasashen yanayin Najeriya ta ce za a fuskanci bahagon yanayi a kasar
Wallafawa ranar:
Kunna - 20:04
Shirin wannan mako zai yi dubi ne yadda Hukumar da ke kula da harkokin hasashen yanayi ta Nigeria, ta yi hasashen samun wani gagarumin sauyin yanayi a yankunan arewa maso gabas da arewa ta tsakiya cikin ‘yan kwanaki masu zuwa. Bugu da kari hukumar, ta bayyana cewa shima yankin kudancin Nigeria zai shiga yanayi na zafin rana da wasu alamun hadari, kana yankunan da ke kusa da ruwa, za su shiga yanayi na hazo da ganin alamun hadari.
Jihohin kudancin Nigeria irin su Lagos, Delta, Rivers da Bayelsa, ana sa ran samun yanayin hadari da tsawa a wadannan kwanaki.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nasiru Sani ............
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu