Ilimi Hasken Rayuwa
An yaye daliban farko da suka koyi aikin likita a jami'ar Damagaram
Wallafawa ranar:
Kunna - 09:55
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' ya yi tattaki zuwa jihar Damagaram Zendir ta Jamhuriyar Nijar ne, inda jami'ar Damagaram ta yaye daliban farko da suka yi karatun aikin likita. A wannan jami'ar, kuma a wannan rana aka gudanar da bikin karrama malaman sashen koyar da kiwon lafiya da suka samu karin girma, sakamakon nasarar da suka yi ta cin jarabawar kwarewar nan ta hukumar kula da kwarewar malaman jami'o'i a nahiyar Afrika.