Dan Jarida Ali Muhammed kan taron ECOWAS don nazarin halin da Nijar ke ciki
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:37
Yau ake sa ran shugabannin kasashen Afirka ta Yamma wato ECOWAS ko CEDEAO su gudanar da taronsu a Abuja, domin nazari akan rahotannin da za’a gabatar musu akan halin da ake ciki a Nijar dangane da juyin mulkin da akayi da kuma kokarin mayar da gwamnatin fararen hula karagar mulki.
ECOWAS ta ce tana daukar duk matakan da suka dace ta fuskar diflomasiya domin warware matsalar, yayin da bangarori da dama ke adawa da daukar matakin soji.
Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da dan jarida mai fashin baki Ali Muhammed Ali akan halin da ake ciki da kuma hasashen da ake yi wa wannan taro, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu