Yayin da lokacin gudanar da zaben shugaban kasa da na gwamnonin Najeriya ke kara karatowa, Kungiyar Kasashen Turai ta gargadi 'yan siyasar Najeriya akan bukatar kauce wa yin kalaman batanci da kuma tinzira magoya bayansu domin tashin hankali.
Kungiyar ta kuma gargadi 'yan siyasar da su kauce wa sanya baki akan ayyukan da hukumar zabe ke yi, domin bata damar gudanar da ayyukan dake gabanta.
Dangane da wannan gargadi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Shehu Abdullahi Zuru na Jami’ar Abuja.
Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu