Tattaunawa da Shehu Zuru kan yadda jihohin Najeriya ke karbo basussuka
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:54
Kungiyar Agaji ta Action Aid a Najeriya ta bukaci hukumomin yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya da su mayar da hankali akan gwamnatocin jihohi saboda yadda suke karbo basussuka a daidai lokacin da wa’adin mulkin su ke gab da karewa. Mataimakin shugaban kungiyar Mac Imoni Amarere yace wasu daga cikin wadannan gwamnoni na karkata basussukan da suka ciwo, yayin da zasu bar wadanda zasu gaje su da matsala.
Dangane da wannan kira, Bashir Ibrahim idris ya tattauna da Farfesa Shehu Abdullahi Zuru, masanin shari’a a Jami’ar Abuja, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu