Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Nick Dazang kan ranakun zaben 2023 da kuma sabuwar dokar zabe
Wallafawa ranar:
A Najeriya hukumar INEC ta sanar da ranakun zaben shugaban kasa da na ’yan Majalisu a 2023 da ta ce zai gudana ranar 25 ga watan Fabarairun yayinda na gwamnoni zai biyo baya a ranar 11 ga watan Maris. Shugaban hukumar Farfesa Mahmuh Yakubu ya sanar da wannan mataki ne bayan shugaba Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan sabuwar dokar zabe a jiya. Kan hakan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon Daraktan hukumar Mr Nick Dazang don jin tasirin wannan sabuwar doka