A yayin da ya rage kasa da makwanni uku a soma gudanar da gasar cin kwallon kafar nahiyar Afrika a kasar Kamaru, shugaban hukumar kwallon kafar nahiyar ta Afrika CAF Patrice Musepe ya ziyarci kasar, a dai dai lokacin da ake jita jitar cewa za a dage gudanar da gasar, saboda dalilan cutar Korona, da ke ci gaba da yaduwa saboda sabon nau’inta na Omicron musamman a nahiyar turai, inda kungiyoyin kwallon kafa suka bayyana cewa, ba za su bar ‘yan wasansu su halarci gasar ba.
A kan haka ne Mahaman Salisu Hamisu ya tattauna da Isma’ila Abba Tangalashi mai sharhi kan wasannin kwallon kafa da ke Kano a Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu