Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Comrade Deji Adeyanju kan cika shekara guda da ENDSARS
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:45
A Najeriya, an cika shekara daya da zanga-zangar EndSars, wadda babbar manufarta ita ce rushe rundunar ‘yan sanda mai yaki miyagun laifufuka, to sai dai daga bisani tarzomar ta kazance tare da lalata kadarorin gwamnati da na al’umma, yayin da aka ruwaito cewa an samu asarar rayuka. To shekara daya bayan faruwar lamrin, Ahmed Abba ya zanta da Comrade Deji Adeyanju, daya daga cikin wadanda suka shirya wannan zanga-zanga, wanda ya bayyana dalilansu na kaddamar da wannan tarzoma.