Bakonmu a Yau
Malisar dokokin Nijar ta bukaci gwamnati ta kwato mata da yaran da Boko Haram ta yi garkuwa da su
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:27
A jamhuriyyar Nijar, bayan da ministan tsaron kasar Kalla Muntari, ya yiwa majalisar dokokin kasar bayani kan yanayin tsaro da yankun Diffa da Tillabery dake fama da tashe tashen hankullan kungiyoyin dake ikararin jihadin musulunci da makama. Majalisar dokokin ta bukaci gwamnati ta gaggauta nemo mata da kananan yaran da ‘’yan Boko-Haram suka sace a Garin Ingalewa da Tumur na jahar Diffa.A kan haka ne, Sule Maje Rejeto ya yi fira da dan majalisar dokokin Lamido Mummuni Haruna, domin jin irin shawarwarin da suka ba wa gwamnatin.