Isa ga babban shafi

Kotu ta bawa EFCC umarnin ci gaba da tsare Bobrisky

Babbar kotun tarayya da ke zaman ta a Legas a Najeriya, ta sanar da ranar 9 ga watan Afrilun 2024 a matsayin ranar da za ta ci gaba da sauraron karar da take yiwa fitacen dan daudun nan Idris Okuneye, wanda aka fi sani da Bobrisky.

Fitaccen dan daudu, Bobrisky kenan
Fitaccen dan daudu, Bobrisky kenan © Premiumtimes
Talla

Hukumar EFCC ce ta gurfanar da Bobrisky gaban kotun, kwana guda bayan bayyanarsa gaban hukumar ‘yan sanda da ke Legas, bisa zarginsa da wulakanta kudin kasar wato naira.

Mai shari’a Abimbola Awogboro, ya ayyana ranar ci gaba da sauraron karar ne, bayan da Bbrisky ya amsa laifuka hudu da ake tuhumarsa da aikatawa.

Kotun ta kuma bayar da umarnin cewa, Bobrisky zai ci gaba da zama a hannun hukumar EFCC har zuwa lokacin da za a yanke masa hukunci.

Hukumar yaki da masu yiwa arzikin Najeriya zagon kasa wato EFCC, ta gurfanar da Bobrisky gaban kuliya ne, bisa zarginsa da aikata laifuka shida, ciki kuwa har da batun wulakanta kudin kasar da kuma zargin almundahanar kudade.

Idan har kotun ta yanke masa hukunci bisa laifukan da ake zarginsa da aikatawa, Bobrisky zai yi zaman gidan yari har tsawon watanni shida ko kuma ya biya tarar naira 50,000, ko kuma ma kotun na iya hada masa wadannan hukunci baki daya a lokaci guda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.