'Yan Afirka ta Kudu na barazanar kai wa 'yan Najeriya hari saboda Super Eagles
Najeriya – Gwamnatin Najeriya ta roki ‘yan kasar ta mazauna Afirka ta Kudu da su kaucewa bayyana farin cikin su a fili idan kungiyar Super Eagles ta samu nasara a kan Bafana Bafana a gasar cikin kofin Afirka dake gudana a Abidjan.
Wallafawa ranar:
Gobe ne ake saran kasashen biyu su fafata domin samun tikitin zuwa wasan karshe na gasar dake ci gaba da dauke hankalin masu sha’awar kwallon kafa a kasashen duniya.
‘Yan Najeriya da dama dake zama a biranen Afirka ta Kudu sun bayyana samun sakonnin barazana daga wasu ‘yan kasar dangane da wannan wasa da za’ayi gobe laraba.
Daya daga cikin shugabannin ‘Yan Najeriyar mazauna kasar Godwin Okeke yace ba a yau suka fara fuskantar irin wannan barazana daga mutanen kasar ba, inda yace ko a shekarun baya da kungiyar kwallon kafa ta matar Najeriya ta je can domin karawa da takwarorinsu na Afirka ta kudu, su da magoya bayan su da kyar suka sha, sakamakon hare haren da aka kai musu da duwatsu saboda nasarar Najeriyar.
Sanarwar da ofishin jakadancin Najeriya dake Pretoria ya gabatar, ya bukaci ‘yan Najeriya suyi taka tsan tsan wajen kalaman su da kuma inda suke shiga domin kaucewa barazanar da wasu bata gari ke yi na kai musu hari.
Ofishin Jakadancin ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da su kaucewa bukukuwa idan kasar ta samu nasara, tare da kuma kira a gare su da su zama masu bin doka da oda a koda yaushe.
‘Yan kasar Afirka ta Kudu sun dade suna kai munanan hare hare a kan ‘yan Najeriya da kuma wasu ‘yan Afirka saboda zargin da suke musu na mamaye harkokin kasuwanci da ayyukan yi, yayin da suke zargin bakin da kuma hada hadar kwaya.
A shekarar 2019 akalla baki 10 aka kashe a Afirka ta Kudu lokacin da wasu batagarin matasa suka dinga kai hari a kan ‘yan kasashen Afirka da kuma wuraren kasuwancin su, abinda ya tinzira shugaban kasa na lokacin Muhammadu Buhari janye jakadan kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu