Najeriya: Ruftawar gini ya kashe wasu yara biyu a jihar Legas
Wasu yara biyu masu suna Gbolahan da Olayinka Atolagbe sun mutu bayan da wani katangar wani gini da ke makwabtaka da su ya rufta a gidansu a unguwar Ikorodu dake jihar Legas.
Wallafawa ranar:
Rahotanni suka ce lamarin ya faru ne a wannan asabar lokacin da ake ake ruwan sama kamar da bakin kwarya a anguwar.
An tsinto gawarwakin yaran biyu ne bayan da kwashe sa'o'i a karkashin baraguzai duk da kokarin mazauna anguwar da suka kai musu daukin gaggawa.
Kakakin hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa reshen Kudu-maso-Yamma, Mista Ibrahim Farinloye, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar.
Jihar Legas ta yi kaurin suna wajen ruftawar gine-gine wanda so tari kan kai ga tasa rayukan mutane.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu