Faransa ta kaddamar da shirin bunkasa harshen Faransanci a Lagos
Yau Faransa ke kaddamar da wani shirin bunkasa koyar da harshen Faransanci a makarantun Lagos da ke kudancin Najeriya, karkashin wata yarjejeniya da za a sabunta tsakanin gwamnatin jihar da karamar ministan raya kasa da dangantaka tsakanin kasashen a Faransa.
Wallafawa ranar:
A ziyarar da ta ke yi yanzu haka Najeriya tun daga ranar 28 ga watan Mayu, uwargida Chrysoula Zacharopoulou ta halarci bikin ranstsar da sabon shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu kafin ta karasa jihar Lagos don aiwatar da shirin koyar da harshen na Faransanci.
Bikin sanya hannu kan yarjeniniyar, wata dama ce ta sake tabbatar da kawancen da aka yi a baya da kuma kaddamar da sabon shirin koyar da harshen Faransaci a makarantun sakandiren gwamnati a zamanance.
Kafin bikin da zai gudana yau a birin Legas, sai da karamar ministan ta Faranasa da ke kula da cigaba da kuma dangantar kasa-da-kasa da kuma raya harshen Faransanci ta kai ziyara birnin Ilori na jihar kwara, inda suka sanya hannun kan yarjejeniyar fahimtar juna da gwamnatin jihar kan ayyukan gona da raya al’adu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu