Isa ga babban shafi

Ci gaba da kasancewar jami'o'in Najeriya a kulle ya na kona min zuciya- Buhari

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya ce ya na matukar samun tashin hankali a game da yadda ake ci gaba da kulle jami'o'in kasar sakamakon yajin aikin kungiyar ASUU ya na mai rokon malaman jami’o’in kasar da su bude makarantu.

Shugaban Najeriya Mohammadu Buhari
Shugaban Najeriya Mohammadu Buhari © Bashir Ahmad
Talla

Shugaban wanda ya bayyana haka a wata zantawa da ya yi da manema labarai a yayin bikin cikar kasar shekaru 62 da samun yancin kai, ya bukaci malaman jami’a da ke yajin aiki su koma ajizuwa, a yayin da ake ci gaba da tattaunawa don lalubo masalaha.

Buhari ya ci gaba da cewa yana jin kuna a cikin zuciyarsa a kan yadda yajin ya ke kawo cikas a kan ilimi mai zurfi a kasar, yana mai shawartar malaman jami’an da su bari a yi amfani da iya abin da Allah ya huwace wa gwamnatin tarayya wajen warware matsalolinsu.

Yajin aikin da malaman jami’a a Najeriya ke yi a halin yanzu ya gurgunta harkokin karatu tun da suka fara shi a ranar 14 ga watan Fabrairun wannan shekarar.

Tun da aka fara wannan yajin aikin ne ‘yan Najeriya da dama ke ta magiya a game da batun warware matsalar, a yayin da kungiyar daliban kasar suka gudanar da jerin gangami don tabbatar da an samu mafita, amma lamarin ya ci tura.

Malaman jami’an suna neman a kyautata yanayin karatu ga dalibai, karin kudaden tafiyar da jami’o’in a kan wanda gwamnati ke samarwa da kuma karin albashi, kamar yadda yake kunshe a yarjeniyoyi da dama da suka kulla da gwamnatin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.