Isa ga babban shafi

An nemi Najeriya ta binciki zargin hadin bakin soji da masu aikata muggan laifuka

Wata hadakar kungiyoyin fara hula a Najeriya ta bukaci shugaba Muhammadu Buhari da ya kaddamar da bincike a kan zargin cewa  wasu jami’an sojin kasar na hada baki da masu aikata muggan laifuka.

Shugaban Najeriya  Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. AFP - LUDOVIC MARIN
Talla

Kungiyar ta ce hakan ya zama wajibi ne bayan kalaman da wasu matasa da suka gudanar da zanga zanga a karamar hukumar Umunneochi  ta jihar Abia, da limamin cocin da aka sace,  Samuel Kanu-Uche suka yi, inda suke zargin wasu bata garin sojoji da hannu a tabarbarewar tsaro a yankin.

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da hadakar kungiyoyi 21 a karkashin jagorancin kungiyar nan mai da’awar mutunta doka, wato,  Accountability Advocacy Centre, Lagos da ke Legas.

Kungiyoyin sun bayyana damuwa ainun, a kan yadda ake ci gaba da zargin sojoji da hannu a matsalar tsaro, suna mai kira da  a gudanar da bincike.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.