Buhari ya baiwa Ministoci masu son shiga zabe umarnin ajiye mukamansu
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya baiwa ministocin sa dake bukatar tsayawa takarar zabe da su aje mukaman su nan da ranar 16 ga watan nan kamar yadda doka ta tanada.
Wallafawa ranar:
Yanzu haka akalla ministoci 10 suka sayi fom din takarar shugaban kasa da gwamna da kuma majalisun tarayya, cikin su har da Rotimi Amaechi da Abubakar Malami da Pauline Tallen
Ministan yada labarai Lai Mohammed ya yi Karin haske akan umurnin, inda ya ce, mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ne kawai wanda umarnin bai shafa ba, a matsayinsa na zababben da jama’a suka kadawa kuri’a.
MInistan watsa labaran Najeriya Lai Mohammed
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu