Mayakan Boko Haram sun kai hari kan garin Geidam
Mayakan Boko Haram sun kai hari kan garin Geidam, da ke jihar Yobe, inda suka kutsa cikin garin a daren Larabar da ta gabata.
Wallafawa ranar:
Jaridar Daily Trust ta ruwaito wasu da suka shaida faruwar al’amarin na cewa, mayakan na Boko Haram sun ajiye baburan nasu ne a wata unguwa nesa kadan da inda suka tafka barna.
Bayanai sun ce ‘ya ‘yan kungiyar ta Boko Haram sun afkawa wasu daga cikin mazauna yankin gabashin garin na Geidam ne, inda suka kona wata makarantar kimiyya da fasaha ta gwamnati, bayan kashe mutum daya a harabar makarantar.
Wata majiyar da Daily Trust ta ruwaito, ta bayyana cewarmayakan na Boko Haram sun kuma kai hari kan wani gidan mata masu zaman kansu a garin an Geidam inda suka kashe mutane akalla 10.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu