Isa ga babban shafi
Najeriya - Katsina

Gwamnan Katsina ya ba da umarnin maida layukan sadarwa a kananan hukumomi 10

Gwamnan Katsina Aminu Bello Masari ya bukaci  hukumar sadarwar Najeriya NCC, da ta dawo da layukan sadarwa a kananan hukumomi goma daga cikin 17 da dokar katse layukan ta shafa, wadda aka kafa kimanin watanni hudu da suka gabata.

Gwamnan JIhar Katsina Aminu Bello Masari.
Gwamnan JIhar Katsina Aminu Bello Masari. © Daily Trust
Talla

Daraktan yada labaran Gwamnan na Abdu Labaran Malumfashi ya ce kananan hukumomin goma da aka maidawa layukan sadarwar sun hada da Matazu, Musawa, Kurfi, Dutsinma, Kafur, Malumfashi, Dandume, Bakori, Funtua, da kuma Danja.

Kananan hukumomin da dokar katse layukan sadarwar za ta ci gaba da aiki kuwa sun hada da  Sabuwa, da Faskari, da Batsari, Safana, Kankara, da Danmusa da kuma Jibia.

Daraktan watsa labaran na Katsina ya ce gwamnati ta yanke shawarar daukar matakin ne sakamakon samun saukin da aka samu na hare-haren ‘yan bindigar da suka adabi jama’a a sassan yankunan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.