Zamfara: Tsaro ya tabarbare a garin Shinkafi
Rahotanni daga Najeriya sun ce Yan bindiga a Jihar Zamfara sun mamaye kauyuka da dama a karamar hukumar Shinkafi, inda suka tare tawagar motocin sufuri, suka kashe mutane da kuma kora wasu cikin daji.
Wallafawa ranar:
Kunna - 04:01
Bayanai daga yankin sun ce yanzu haka wadannan Yan bindigar na iko da wasu kauyuka da dama.
Wannan ta’asa da ‘yan bindiga ke aikatawa na faruwa ne duk da matakan da hukumomin kasar suka dauka don sama wa al’umma sauki.
Majiyoyi daga yankin sun ce ko a makon da ya gabata, wadannan barayin daji sun ci karensu ba babaka, inda suka kwashe kwanaki 6 a jere suna da kisa da dibar mutane.
Kan haka ne Michael Kuduson ya tuntubi wani dan asalin garin Shinkafi, Hamdai Alhazzai Shinkafi, kuma ga tattaunawarsu
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu