An tsinci gawarwakin wasu 'yan Nijar 7 a Lagos
A Najeriya, an tsinci gawarwakin wasu 'Yan asalin Jamhuriyar Nijar guda 7 da ke zaune gida daya a unguwar Alaba da ke birnin Legas da sanyin safiyar wannan Lahadi.
Wallafawa ranar:
Bayanai sun ce ba wasu alamun raunuka a jikin mutanen 7 da suka mutu, wadanda tuni aka yi masu jana'izarsu tun da safiyar, bayan sanar da 'yan sanda faruwar lamarin.
Shugaban 'Yan Nijar mazauna Legas Alhaji Sa'idu Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin, to saï dai kawo yanzu ba a gano dalilin mutuwar mutanen 7 ba, inda ya ce tuni suka sanar da mahukunta ciki har da ofishin karamin jakadan Jamhuriyar Nijar da ke Legas.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu