Najeriya - Tsaro
An kashe Malami da Dalibi a wani kwaleji dake Lagos
Rahotanni daga Lagos dake Najeriya na cewa wasu ‘yan bindiga sun harbe wani malamin jami’a da dalibi a kwalejin Ilimi na Michael Otedole dake karamar hukumar Epe a jihar.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni suka ce an kashe malamin mai suna Ahmed Saheed a yankin Poka yayin da dalibin mai suna Razak Bakare ya gamu da ajalinsa cikin dakin kwanan dalibai.
Majiyar ‘yan sanda tace mummunar lamarin ya faru ne sa’o’i 48 tsakaninsu da juna, wato tsakanin ranakun Laraba da kuma Jumma’a.
Wani dan majalisa da ba saraken yankin sun tabbatar da aukuwar lamarin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu